WASIKA ZUWA GA MATASA MASU AIKATA ISTIMNA'I

Share:

ma'anar ISTIMNA'I shine= fitar da mani ko sha'awa da gangan ta hanyar da bata dace ba.

Matasa Maza da mata, suna neman taimako akan illolin da suke samu a jikunansu sakamakon Istimna'i wato Masturbation. An kawo hujjoji
gamsassu daga Al-Qur'ani da Sunnar Ma'aikin Allah (saw) da fatawoyin Amintattun Malamai duk akan HARAMCIN ISTIMNA'I, Amma duk da haka wasu matasan basu yarda sun dena ba.

Wasu kuwa sunji tsoron ALLAH sun riga sun dena, bubban dalilin da yake janyo musu afkawa cikin
wannan bala'in shine :

1. Kallon Fina-finan batsa.

2. Shiga shafukan internet na batsa.

3. Yin zantukan batsa tsakanin
saurayi da budurwa.

4. Kusantar zina ta hanyar kallo da
shafa, ko zance da dai sauransu.

Wasu kuma suna aikata hakan ne
dan gudun afkawa ZINA, basu san cewa shi d'inma ZINAR bane!!

Idan kun Qi bari domin Allah, to ku dubi irin illolin da yake haifar muku ajikinku mana!!!

1. MUTUWAR IDANU.

2. MUTUWAR AL'AURA.

3. CIWON BAYA.

4. BUGAWAR QIRJI.

5. RIKICEWAR TUNANI.

6. YAWAN MANTUWA.

7. KARANCIN 'YA'YAN MANIYYI.

8. SAURIN INZALI.

9. SHAFAR ALJANU, ETC.

Wad'annan 'yan kad'an ne daga cikin Matsalolin da ISTIMNA'I yake haifarwa. kuma duk wanda bai tuba ya dena ba, idan ya mutu a haka zai je ya tarar da hisabi.

DAN GIRMAN ALLAH!! Matasa ku kiyayi zina da duk dangoginta, ku Qaurace ma duk wani abinda zai rinQa motsa muku sha'awa, idan
da hali kuje kuyi aure, idan kuma babu hali, to ku yawaita azumi.
ALLAH YA SAUWAQE.

Don Allah 'Yan uwa MAZA DA MATA,
DON ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar Sharing a FACEBOOK, TWITTER, BBM WHATSAPP, da sauransu. Insha Allahu wasu da yawa zasu amfana.
Manzon Allah (s.a.w) yace: "WALLAHI IDAN ALLAH YA SHIRYAR DA MUTUM GUDA TA
DALILINKA, YAFI ALKHAIRI GAREKA FIYE DA ABAKA JAJAYEN RAQUMMA"
Wani mutum yazo wajen manzon Allah S. A.W. ya ce: Yah-Manzon-rahma zan tambaye ka rayuwar duniya da ta lahira.

1.  Yah Manzon Allah ina son in zama mafi sani a cikin mutane?
AMSA
Sai ya ce "Ka ji tsoron Allah ka bi dokokin Sa."

2.  Ina son in zama mafi arziQi a cikin mutane?

AMSA

sai ya ce "Ka zama mai wadatar zuci."

3.  Ina son na zama Wanda yafi kowa acikin mutane?

AMSA

Sai ya ce "Ka zama mai amfanarwa."

4.  Menene zai kare ni daga wuta?

AMSA

Sai ya ce "Ka zama mai yawan yin Azumi."

5.  Ina so in zama mafi adalci a cikin mutane?

AMSA

Sai ya ce "Ka so ma d'an uwanka abin da ka ke soma kanka."

6.  Ina son in zama mafi amfanin mutane a wajen Allah?

AMSA

Sai ya ce "Ka yawaita tuna Allah."

7. Ina son imanina ya zama ingantacce?

AMSA.

Sai ya ce "Ka gyara halayen ka."

8.  Menene yake huce fushin Allah  (S.W.T.)?

AMSA

Sai ya ce "Ba da zakka a boye da kyautata ma 'yan uwa."

9. Wani zunubi yafi muni awajen Allah?

AMSA

Sai ya ce "Mummunar hali shine rowa"

10.  Ina so in zama mafi biyayya ga Allah?

AMSA

Sai ya ce "Ka bi umurnin Allah za ka zama mafi rinjaye a wurin Allah."

YA ALLAH Ka sa mu gama da Duniya lafiya.

INA ROQON MAI KARATU dan GIRMAN ALLAH DAN SON ANNABI kayi Qokari ka tura wani group d'in domin tunasarwa.

6 comments:

  1. Enter your comment... peace be upon you

    ReplyDelete
  2. Allah ubangiji kaji kanmu ubangiji Allah ya gafarta Mana zunuban mu ubangiji Allah yasa mu amfana da nasihannan ya ubangiji Allah ka tsaremana xukatan mu ya ubangiji Allah kasa mu guji aikata sharri Allah yasa mu dace amee.

    ReplyDelete
  3. allah yabiyaki, to idan mutun yasamu wadannan matsalolin menene magani

    ReplyDelete
  4. Enter your comment... Allah ya tsare mana imaninmu

    ReplyDelete