zuciyarmu daya 1

Share:
_ZUCIYARMU 'DAYA_ .* 漏Mamuh geee For you my
*zinnie* _Bismillahir-rahamanir raheem._ 1-2 Zaune
take Bakin gadon da abbanta ke kwance yana jinya
tsawon shekara biyu. Hawaye ne kwance a fuskarta
wa'inda zubowarsu sun zame mata azaliya. Shekarar
abbanta biyu a kwance rigis yana jinya, Ita ke
jinyarsa,ita ke aikin Samar da abibda zasuci duk da
qananun shekarunta da basu haura sha bakwai ba.
Kallon 'dakin dasuke ciki tayi Babu komai aciki banda
ru6a66iyar katifar da abbanta yake kai Wanda har
gwara tabarma da ita sbd dadewarta dakuma dadewar
da abban yayi kwance akanta. Ginin gidan nasu da
'dakunan gidan gabaki daya sun farfashe alamun ko
wane lokaci zasu iya ruguzowa. Share hawayenta tayi
da yagaggiyar atampar jikinta ta miqe zata fita
ahankali abbanta yayi magana bataji mai yaceba saita
dawo ta zauna tareda kara kunnanta kusa dan taji
maiyake fada. JIDDAH kici gaba dayimin addua Allah
ya bayyanamin 'dan uwana kafin nabar duniya. Sabbin
hawaye suka zubo mata tace, Abbah dan Allah kadaina
maganar daddyn lokoja tunda baidawoba kuma kai ba
lafiyane dakaiba. Hawaye yafara yana fadin, Jiddah
inason damqaki a hannun amanane kafin nabar duniya,
Nasani bakida kowa saini,kuma yanda muke dinnan
idan na tafi nasan kyararki za'a dinka sbd bakida kowa
kuma anai mana kallon almajirai. Kuka tasaki mai cin
rai tana fadin, Abbah dan Allah kadaka barni tunda
Kasan halinda zan shiga idan katafi, Tun yanxu ana
qyamata ana hantarata duk inda naje Idan katafi
bansan yazanyi ba. Tsit 'dakin yayi sai sheshekar
kukanta dake tashi, shima abban nata hawaye yakeyi.
Sundau awa 'daya ahakan kafin ta miqe ta fito tsakar
gidansu ta fada 'dakin innarta ta dauko sauran kokon
goman data siyowa abban takawo masa ya kurba
kadan yace tilas ita ta kurba ko yayane sbd yasan
batashaba dan wani lokacin takan kwana biyu ta yini
batasha ko taci wani Abu ba sbd basudashi kuma
basuda mai basu. Kofin ta wanke ta jawo kujera ta
zauna bakin qofar 'dakin tareda rafka tagumi.
*************** ASALIN LABARI Ibrahim buba shine
cikakken sunan mahaifinta. Ibrahim marayane datun
yana yaro mahaifinsa ya raso sai ya taso dagashi sai
mahaifiyarsa inna mero. Ibrahim yataso cikin gata da
kulawa sbd inna mero tana sana'arta ta cikin gida dan
haka ta maida duk wani samunta gurin kula da 'danta
Ibrahim sbd shikadai gareta har mijinta yarasu. A
makaranta Ibrahim ya hadu da Abdulhameed 'dan
dagacin qauyensu. Sannu ahankali abotarsu tayi nisa
sbd halinsu dayazo daya na Neman magana da rashin
ji amakaranta. Abdlhamid shima shi kadai mahaifansa
suka haifa, Mahaifiyarsa ta jima da rasuwa mahaifinsa
kawai yarage masa shima babansa yadauki son duniya
ya dora masa. Tsananin son da iyayensu ke nuna musu
shiya bada gudunmawa gurin sangarcewa da fara
lalacewarsu a qauyen dan tuni suka fara iya tadi da
'yanmata. Suna ss 2 a secondary Allah ya karbi ran
baban Abdulhameed sakamakon guba da aka sanya
masa a abinci sbd son kar6e kujerarsa ta mulkin
dagacin gari. Bayan kwana biyu da rasuwarsa aka
kuma shirya yanda za'a kashe Abdulhameed Allah yasa
yaji cikin dare ya tattara iya dukiyar babansa daya gani
ya gudu. Bugun gida sukaji tsakar dare
gagararsu yakeyi ga kuma karatunsu yana neman
lalacewa. Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫 [19:16,
1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱
*_ZUCIYARMU 'DAYA_ .* 漏Mamuh geee For you my
*xinnie* _Bismillahir-rahamanir raheem_ . 3-4 Fadi
tashi inna mero tafara dan batason karatunsu ya lalace
bare taga sunason karatun sosai. Sanar qosai tafara
amma Sam 'dan cinikin bazai yi lalurar
makarantarsuba. Canza Sana'a tayi zuwa ta waina
nanma babu wani abin kirki, Qarshe dai aikin sharar
makarantar secondary din dake qauyen tasamu inda
duk wata ake bata dubu hudu, Zuwa tayi ta roqi
principal akan ahada kudin aikinta na wata uku riqe
abari 'yayanta suyi jarabawa. Haka kuwa akayi
harsuka rubuta jarabawar gama secondary suka dasa
wani zaman banxar agida sbd babu abin cigaba da
karatun nasu. Shiryawa inna tayi taje qauyensu dasuka
baro ta siyar da 'dan akurkin gidanta tadawo tabawa
maqwabcinsu dake aikin photocopy a jami'ar birni
yasiyo musu jamb form yacika musu. Da lokacin
jarabawar jamb yayi yatafi dasu birni sukayo suka
dawo. Tunda suka dawo suke shirya yanda zasuyi idan
suka fasa birni suka hadu da wayayyun yan mata.
Alhmdullillah sunci jarabawa kuma sun samu
admission inda suke karantar law dukkansu. Sauran
kudin gidan sune dama inna ta aje dasu sukayi
registration da komai dasuke buqata. Karatu yayi nisa
dan tuni 'yayan inna suka waye suka zama cikakkun
gayu sbd sun hadu da abokanai 'yayan masu kudi ga
yan mata wayayyu sun samu sbd dama dukkaninsu
babu baya agurin kyau irin na asalin Fulani. Inna tsuf

No comments